Mai dad'i, kuma dad'in wannan lada ya mantar da shi d'acin hak'urin da yayi cikin mawuyacin halin da ya tsinci kansa. 7. Daukar shawarar da Annabi (s.a.w) ya bayar a ingataccen hadisin nan yana daga cikin abubuwan da suka fi komai amfani a wannan fage. Ga dai abinda yake cewa: "KU RIK'A LA'AKARI (A ABUBUWAN DUNIYA) DA WAD'ANDA KUKA FI, BA DA WAD'ANDA SUKA FI KU BA; DOMIN WANNAN SHINE BABBAN ABINDA ZAI HANA KU RIK'A GANIN ALLAH BAI YI MUKU WATA NI'IMAR KIRKI BA". Bukhari da muslim ne suka rawaito shi. Don hak'ik'a idan bawa ya sanya wannan mahimmin ma'aunin a ransa zaka ga duk yadda yake, yafi mutane da yawa lafiya da arzuki da abubuwan da suke da alak'a da su. Ta haka sai damuwa,bak'in ciki da k'uk'umi da suke nema su kai shi k'asa sun gushe, farin cikinsa kuma ya k'aru, yayi ta murna, ganin cewa ya zarta matane da yawa a ni'imomin da Allah yayi musu gaba d'aya. Kuma a duk lokacin da mutum yayi zurfin tunani a kan ni'imomin da Allah yayi masa, na fili da na b'oye, da na addini da na duniya,to lallai zai ga ubangiji ya ba shi alheri ba kad'an ba,ya kuma kare shi daga sharruka masu yawa. Ba shakka irin wannan yana ije bak'k'an ciki, yana kuma sa zuciya ta yi fari fat; ta cika da farin ciki. FASALI (3) 8. Daga cikin abubuwan da suke kawo farin ciki, su kuma gusar da bak'in ciki da k'uk'umi, k'ok'arin gusar da ainihin abinda ya janyo wannan bak'in cikin, da kuma dogewa wajen samar da abubuwan da ke kawo farin cikin na farko dai ya san cewa abin da kawai ya wuce ya wuce, kuma ya sani cewa yana daga wauta da hauka da rashin aikin yi ya zauna yayi ta tunani a kan wannan abinda ya same shi, tunda dai aikin gama ya gama. Don haka ya daure yafi k'arfin zuciyarsa ya daina tunani akan abin, ya kuma yi k'ok'ari ya daina damuwa da sak'e sak'en zuciyarsa take masa na abubuwa da suka shafi rayuwarsa ta nan gaba, kamar ta rik'a masa cewa ta yiwu talauci ya same shi, ta yiwu wani abin tsoro ya afka masa, da dai shauran irin abubuwan da mutum yake tsoron su same shi a rayuwarsa ta duniya. Ya san cewa ba wanda ya san abinda zai faru nan gaba sai Allah, kuma duk abinda zai kasance a wannan lokaci mai zuwa na alheri ko na sharri,mai dad'i ko mara dad'i a hannun Allah yake Buwayi Gagara misali, Mai matuk'ar hikima a duk abinda ya hukunta. Abin da kawai bayi suke iya yi su yi k'ok'arin ganin sun samu alheri dake cikinsa, sun kuma ije sharri da ya k'unsa. Kuma bawa ya san cewa matukar zai daina fargaba da sannu damuwa akan makomar rayuwarsa, ya mik'awa ubangiji al'amarinsa yana mai nutsuwa da fatan ya rufa masa asiri, matuk'ar zai yi haka, to zaka ga zuciyarsa ta nutsu,kuma abubuwa sun dai daita, bak'in ciki da damuwa kuma sun kama gabansu. 9. Daga abinda yake kan gaba, yin wannan addu'ar da Annabi(s.a.w) shi da kansa ya kasance yana yinta, wannan addu'a kuwa itace: YA ALLAH KA GYARAMIN ADDINI NA WANDA SHINE K'ASHIN BAYAN AL'AMURANA,KA KUMA GYARA MIN DUNIYATA WADDA A CIKINTA ABINCINA YAKE, KA GYARAMIN LAHIRATA WADDA NANCE MAKOMA,KA SANYA RAYUWA K'ARIN DUK WANI ALHERI NE A GARENI, MUTUWA KUMA HUTU CE A GARENI DAGA DUK WANI SHARRI" (Muslim ne ya rawaito shi). Haka nan wannan addu'a: YA ALLAH DA RAHAMARKA KAD'AI NAKE SA RAI, DON HAKA (INA ROK'ON) KAR KA BARNI DA KAINA DAI DAI D K'IFTAWAR IDO, KA KUMA GYARA MIN GABAD'AYAN AL'AMURANA, BA WANI ABIN BAUTAWA DA GASKIYA SAI KAI".(Abu Dauda ne ya rawaito shi da isnadi ingantacce). Idan har bawa ya tara hankalinsa wuri guda, yayi da gaske, yayi ta yin addu'a ba k'ak'autawa kan Allah ya gyara masa makomar rayuwarsa ta addini da ta duniya, ya kuma tashi tsaye kan ganin hakan ya tabbata, to Allah kuwa zai cika masa burinsa, kuma bak'in cikin da ya dame shi ya koma farin ciki. FASALI(4) 10. Daga cikin abubuwan da suka fi komai amfani wajen gusar da damuwa da bak'an ciki, idan mutum ya tsinci kansa a cikin masifu k'ok'arin yaga ya rage musu k'arfi. Yadda zai yi kuwa shine: ya d'auka cewa halin da zai samu kansa a ciki a nan gaba, kuma idan hakan ta faru ga yadda zai yi ya daure,ya shanye wannan abu. Idan yayi haka,sai kuma ya ba da k'ok'ari wajen ganin sauk'ak'a abin da zai yi na halin da ya samu kansa a ciki daidai gwargwado. To sakamakon waccan dauriyar da yake shirin yi, da wannan k'okarin da yake yi a yanzu, sai kaga bak'k'an cikinsa sun gushe, maimakon haka kullum k'oka'rinsa shine ya samarwa kansa abubuwan da za su amfane shi, da maganin wad'anda zasu cuce shi, matuk'ar basu fi k'arfinsa ba. Idan abubuwan da suke haifar da tsoro, ko cutuka,ko talauci suka afka masa ko kuma ya rasa wani abu daga cikin ire iren abubuwan da yake so, to ya fuskance su cikin nutsuwa da dauriya. Kai yama yi shirin ko da sun fuce yadda yake tsammani ga irin juriyar da yake shirin yi, domin mutum ya sab'awa kansa da dauriya akan abubuwan k'i kan gusar da tsanani da yake k'unshe a cikinsu, ya kuma ji sun zo masa cikin sauk'i, musamman ma idan ya shagaltar da kansa da yak'arsu matuk'ar iyawarsa. Sai kaga ga dauriya, ga tashi tsaye akan abinda zai amfane shi duk sun had'u.

RAYUWA: RAYUWA: Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai ma...

RAYUWA: RAYUWA: Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai ma...: "RAYUWA: Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai matukar ji...: 'Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai matukar jin k'ai Dukkan yabo ya tabb..."

RAYUWA: Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai matukar ji...

RAYUWA: Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai matukar ji...: "Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai matukar jin k'ai Dukkan yabo ya tabbata ga Allah,wanda dama shine yabo ya cancance shi. Kuma ina mai..."

RAYUWA: Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai matukar ji...

RAYUWA: Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai matukar ji...: "Da sunan Allah mai matuk'ar rahama mai matukar jin k'ai Dukkan yabo ya tabbata ga Allah,wanda dama shine yabo ya cancance shi. Kuma ina mai..."

RAYUWA: HANYOYIN DA SUKE KAIWA ZUWA GA KYAKKYAWAR RAYUWA

RAYUWA: HANYOYIN DA SUKE KAIWA ZUWA GA KYAKKYAWAR RAYUWA

HANYOYIN DA SUKE KAIWA ZUWA GA KYAKKYAWAR RAYUWA

Wannan misalin kuwa shine: hak'ik'a shi dai addini yana kira da babbar murya cewa kowa ya zama yana da wadatar zuci, dangane da arzuki, falala da karimci iri iri da Allah ya raba ya bawa kowa. Ka ga dai shi mumini gaskiya,idan aka jarrabeshi da rashin lafiya ko talauci da makamantansu daga cikin abubuwan da ka iya samun kowa sai ka same shi warkan ba abinda ya dame shi, saboda imaninsa, da wadatar zucinsa da yardarsa da abinda Allah ya bashi. Baya hank'oron abinda ba 'a k'addara masa ba. Yana duban wanda yake k'asa da shi, baya duban wanda ke sama da shi. Kai watakila ma sai kaga farin ciki, walwala, da watayawar da yake ciki ya kere wanda ya samu dukkan abubuwan da yake nema na duniya matuk'ar dai ba a bashi wadatar zuci ba. Kamar yadda zaka samu shi wannan da ba ya tafi da ayyukansa bisa doron imani, idan aka d'an jarrabe shi da talauci, ko rashin wani abin da yake so na duniya, sai ka same shi cikin wani irin tashin hankali da mummunan hali. Ga k'arin misali: idan aka shiga halin tsoro, ko kuma wasu rigimgimun duniya suka yi wa mutum ca, sai kaga mai ingantaccen imani ko a jikinsa. Gabansa ko faduwa ba yayi, gashi a nutse, yasan duk yadda zai b'ullowa wannan lamari da ya tinkaro shi da duk abinda Allah ya hore masa na tunani da magana da aiki, ya daure wannan abin tashin hankalin da ya afka masa. La shakka irin wad'annan ta'adu na hutar da mutum, su kuma tabbatar masa da zuciya. Kamar yadda zaka samu wanda bashi da imani, kwata kwata ya sab'a da wancan. Da wasu ababan tsoro sun faru duk sai ya bi ya canza, hankalinsa ya dugunzuma, tunaninsa ya tarwatsa, ya cika da tsoro da tararrabi, ya shiga cikin tsoro da damuwar da basu misaltuwa. Ire iren wad'annan mutane in basu da wasu d'abiu na halitta da za su taimaka musu, duk sai kaga sun fita daga cikin hayyacinsu, duk sun bi sun k'are sun lalace; saboda basu da imanin da zai hak'urtar dasu musamman ma a cikin da ke sa mutum ya kasa zaune ya kasa tsaye. Mutumin kirki da fajiri, da kuma mumini da kafiri, dukkanninsu suna tarayya wajen koyon jarumta da kuma yadda zasu sauk'ak'awa kawunansu ababan da ake gudun afkuwarsu. Sai dai mumini ya fita daban; saboda k'arfin imaninsa da hak'urinsa, da tawakkalinsa ga Allah,da kuma dogaronsa gareshi,da kuma neman lada a gareshi. Duk wad'annan abubuwa ne da jarumtarsu zata k'aru ta hanyarsu, za kuma ta sauk'ak'a masa tunanin bak'in ciki da sauran masifu. Kamar yadda Allah ta'ala yace: "IN HAR KU(MUMINAI) KUNA JIN RAD'AD'I TO SUMA (KAFIRAI) SUNA JI KAMAR YADDA KUKE JI, KUMA KU KUNA SA RAN SAMUN ABINDA SU BASA SA RAN SAMUNSA A WAJEN ALLAH(WATO ALJANNA)". (Nisa'i 104) kuma kaga suna samun taimako na musamman daga Allah mad'aukaki, wanda zai tarwatsa musu duk wasu ababan da suke tsoro. Allah Ta'ala yace: "KUMA KUYI HAK'URI, DON HAK'IK'A,ALLAH YANA TARE DA MASU HAK'URI". (Anfal 46). {2} Hakanan daga abubuwan da suke gusar da bakin ciki da damuwa : kyautatawa mutane da furuci ko da aiki, da dai sauran nau'o'in kyawawan ayyuka da ta'adu. Dukkannin wad'annan abubuwan alheri ne da ihsani,kuma duk wanda yake aikatasu mutumin kirki ne ko mutumin kawai, za a kare shi daga bak'an ciki iya gwargwadon yadda yake kyautatawa bayin Allah. Sai dai mumini zai rabauta sama da kowa, kamar yadda yake bambanta da cewa shi kyautatawarsa don Allah yake yi da kuma neman sakayyarsa. Sai Allah ya sawwake masa kyawawan ayyuka saboda alherin da yake fatan samu (daga Allah) ya kuma kareshi daga abubuwan da yake k'i saboda ihilasinsa,da neman sakayyarsa daga Allah(shi kadai). Allah Ta'ala yana cewa: "BABU ALHERI A CIKIN YAWANCIN GANAWAR DA SUKE YI IN BANDA WANDA YAYI UMARNI DA SADAK'A KO WANI KYAKKYAWAN AIKI,KO SASANTAWA TSAKANIN MUTANE. KUMA DUK WANDA YA AIKATA WAD'ANNAN ABUBUWAN(DA AKA AMBATA) TO ZAMU BASHI LADA MAI MATUK'AR GIRMA".(nisa'i 114) kaga sai Allah Ta'ala ya bayyana cewa ba wata tababa gabad'ayan wad'annan abubuwa da aka ambata alheri ne daga duk wanda suka fito. Kuma (aikata) alheri,alheri yake kawowa,ya kuma kad'e sharri.kuma lallai duk muminin da ke neman sakayyarsa a wurin Allah to ba shakka Allah zai bashi lada mai matuk'ar girma. Wani daga cikin jimillar wannan babban lada shine gushewar bak'in ciki da abubuwan da ke gurb'atawa mutum rayuwa da makamantansu. FASALI{2} 3. Daga cikin abubuwan dake zama riga kafin damuwa da tashin hankali da yawan tunani akan rigingimun duniya, mutum ya shagalta da kansa da wani aiki ko wani ilmi mai amfani; saboda wannan zai d'auke masa hankali daga tunani akan wannan abinda yake nema ya dagula masa lissafi. Kai ta haka ma watakila sai ya manta da abubuwan da suka janyo masa wannan bak'in ciki da tashin hankali, sai ransa yayi fari, kuma karsahinsa ya k'aru. Wannan sababin har walau mumini da wanda ba mumini ba sunyi tarayya a cikinsa,sai dai shi mumini ya sha bamban da sauran , saboda imaninsa,ihilasinsa, da kuma ladan da yake sa ran samu a wajen Allah lokacin da ya shagalta da kansa da wannan ilimin da yake koya ko yake koyarwa, ga shi kuma abinda ya sani na alheri yana